Video Yadda Wani Ɗan Ƙasar Indiya Ya Rasa Ransa Bayan Ya Goyi Bayan Ɓatanci Ga Annabi Muhammadu (s.a.w)


Rajasthan, Indiya - Kanhaiya Lal, wani mutum 'dan kasar Hindu ya rasa ransa a Rajasthan da ke Indiya bisa zarginsa da goyon bayan wanda yayi batanci ga Annabi Muhammad.

 A ranar Talata, wasu maza biyu da suka zo masa a matsayin kwastomomi sun kai farmaki gami da halaka Lai, wanda tela ne yayin da yake aunasu a shagonsa da ke anguwar Udaipur.

An yi bidiyon wanda lamarin ya auku dashi yayin da aka halaka shi tare da dorawa a yanar gizo. Kamar yadda BBC ta ruwaito, makasansa sun yi ikirarin cewa sun yi hakan ne don daukar fansa a kan mutumin bisa marawa maganar Nupur Sharma, wanda kakakin jam'iyyar Bharatiya Janata ta kasa ne (BJP), wacce ta janyo cece-kuce a kan Annabi Muhammad.

 DUBA: Bibiyemu a HAUSACONNECT.COM don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye a shafin intanet.

 An gano yadda Sharma ya yi furucin, wanda ake gani a matsayin laifi kan Annabi Muhammad yayin wata muhawara a watan Mayu. An zargi Lal da yin wata wallafa a shafin sada zumuntar zamani tare da marawa furucin Sharma. 

Foreign Newspaper ta bayyana yadda aka gano biyun da ake zargi a bidiyon gami da kamasu, Haka zalika, gwamnatin Indiya ta dakatar da amfani da yanar gizo na wani lokaci tare da haramta dandazon taro.

Post a Comment

Previous Post Next Post