Abba Kari, Joshua Dariye, Jolly Nyame: Asiri Ya Tonu Bayan Kaiwa Gidan Yarin Kuke Hari


Majiyoyi sun ce mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Abba Kyari da abokan harkallarsa da ke wurin, mai yiwuwa sun tsere daga magarkama.

Shi ma haka tsohon gwamnan jihar Filato Joshua Dariye da takwaransa na Taraba Jolly Nyame da majalisar kasa ta yi wa afuwa a baya-bayan nan.

Har yanzu gwamnatin tarayya ba ta aiwatar da sakin su Dariye ba har aka samu akasi aka kai hari magarkamar. 

Majiyoyi a cikin magarkamar sun shaidawa jaridar cewa baya ga manyan fursunonin, wasu 'yan ta'adda da sauran masu laifi sun tsere yayin da maharan ke luguden wuta.
 
Sai dai har zuwa lokacin da hada wannan rahoto, babu wani tabbaci a hukumance kan adadin wadanda suka tsere da bayanansu, haka nan BluePrint ta ruwaito.

Wata majiya ta shaida wa jaridar cewa zai yi wuya a iya tabbatar da ko an kwashe Kyari da mutanensa domin kare rayukansu kafin maharan su samu shiga wurin.

Majiyar ta kuma ce haka nan ga tsofaffin gwamnonin da ke daure a magarkamar.

 Ba a samu jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na hukumar kula da gyaran fuska ta Najeriya, Francis Enobore da karamin jami’insa, Mista Humphrey Chukwuendo.

 Wani jami’in da ya so a sakaya sunansa ya ce har ya zuwa karfe 09:30 na safe ba a san inda Kyari yake ba, rahoton Punch.


Post a Comment

Previous Post Next Post