Istimna'i: A Ba Ni Addu'ar Dainawa


Matsalar matasan wannan zamani shi ne son dora wa kansu abin da ya fi karfinsu, sun dage suna bin zugar Shaidan na lallai sai sun auri mace mai kyau, mai wayewa, wacce ta iya gayu da rangwada, maimakon su nemi mai hankali da tarbiyya kuma mai saukin aure su raya Sunnah su yi maganin matsalarsu.

Su wadancan ’yan matan da kuke kwadayi kudi suke so kuma ko kun kashe masu kudin ba lallai su aure ku ba.

Yarinya ko talla take yi in ka bincika ka ji tana da hankali kuma iyayenta mutanen kirki ne shi ke nan sai ka je ka yi aurenka a saukake ka mance da kyalkyal-banza.

Ka sani cewa aure mai sauki shi ne mai albarka kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya sanar mana.

Maganar cewa ba zai iya yin azumi ba saboda aikinsa na tsayuwa, ka sani cewa, Manzon Allah (SAW) ya yi umarni da yin azumi don dakushe kaifin sha’awa ga matasa, yana sane da cewa wadansu aikinsu na wahala ne wadansu aikinsu na sauki, don haka wannan ba hujja ba ce ta kin yin aiki da umarnin Manzon Allah (SAW).

Wannan hudubar Shaidan ce kawai don ya yaudare shi ya ci gaba da aikata sabon da yake aikatawa.

Dama dole ya ji wahala a farkon yin azumin, amma da ya saba zai zame masa jiki ba zai ji wata wahala ba kuma.

Azumi ana iya yin sa da kowane irin aiki kuma duk wanda ya karfafa niyyarsa ya nemi taimakon Allah, Allah zai taimake shi Ya ba shi damar yin azumin a kowane irin hali yake.

Lallai wannan aboki ya sani yin azumi ya fi masa sauki a kan dabi’ar da ya rika lokacin kwanciya.

Shawarata a nan ita ce ko dai ya yi azama, ya nemi taimakon Allah Ya yi aure ko kuma ya kama azumi ka’in-dana’in.

Sai mako na gaba in sha Allah, da fatar Allah Ya sa mu kasance cikin kulawarSa a koyaushe Amin,

Post a Comment

Previous Post Next Post